Allah Sarki: Wasu Malamai Mata Uku Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kaduna.

 Allah Sarki: Wasu Malamai Mata Uku Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kaduna.












Allah Sarki: Wasu Malamai Mata Uku Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kaduna.

Wasu Malamai Mata Uku Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kaduna.

 

An jefa daukacin ma’aikatan makarantar Shehu Idris College Of Health Science & Technology (SIIHST) Makarfi da ke jihar Kaduna cikin alhini sakamakon rasuwar wasu malamai mata uku.

 

AInside Arewa Media, Ta rawaito Malaman sun mutu ne a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a Gwargwaji, a Zariya a yammacin ranar Litinin, 30 ga watan Mayu, a hanyar su ta dawowa daga aiki.

Wadanda suka rasun an bayyana sunayensu da Mrs Adanna Joan Nwafor, babbar jami’a a Sashen Kimiyar Kiwon Lafiyar Al’umma, Mrs Amina Tahir, Ma’aikatar Kimiyar Kiwon Lafiyar Al’umma da Madam Rabi’atu Malami Dogo, babbar jami’a a sashen kula da hakora.

 

Malama ta hudu mai suna Misis Kafayat Abdulrashed ta Sashen MIT ta tsira kuma a halin yanzu tana jinya a asibiti.

Post a Comment

0 Comments