A duk lokacin da kake tashin iskanci, mutane suna maka nasiha ka dena sai kaki denawa, aka koma yi maka mummunan addu’ah to ba zaka wanye lafiya ba, kuma ba zakayi lasting ba Shaidanin yaron nan Mista 442 yayi tashen iskancinsa sosai, ya boye kansa a hotel, daga karshe Allah Ya jefashi a komar mahukuntan Kasar Nijer suka kamashi suka tura gidan yari....







Yau ga wannan ‘yar is_kan yarinya Murja Ibrahim ‘yar TikTok, itama tabi sahunsa, kwana sai gidan yari


 


Muna fatan Allah Ya sa su shiryu a gidan yarinyar, idan ba zasu shiryu ba Allah Ya sa sun tafi kenan


Matsalar da yanzu mata ke fuskanta shine tantance wanda ke sonsu da aure da kuma wanda ke sonsu don sha’awa kawai.

Irin wannan matsalar da ana ganin kamar maza wa’enda suke yan boko zallah ne suke da wannan Ɗabi’ar, a’a ba haka bane musamman a yanzu har da wa’enda ake gani ustazai ne masu addini.


 


Wannan matsalar ba iya mata yan boko zallah bane ke fuskanta, har da mata masu addini suna cikin wannan jarrabawa, saɓanin da ana gani ai mata yan boko zallah masu ra’ayi su suke ake wa soyayyar sha’awa Saboda shigar su na sutura mai bayyana surar jiki.

Kusan idan kana jin korafi sai ka rasa me yake shirin faruwa a wannan zamanin, yadda ɗabi’a da ba namu ba ko a al’adance bare kuma addini amma yanzu muke shirin runguma hannu bibbiyu.


Kusan matasan mu game da lamarin junansu in anzo nan duk imanin mutum sai a hankali a cikin kashi dari, sai an samu 60 ko 70 da za su fadi jarrabawa.


Yakamata mata a ƙara ta’ka tsansan da kuma addu’a sosai da kama kai, matukar maza suna samun da sunan soyayya suna taɓa jiki har ma wani lokacin ya wuce zuwa ga har biyan bukata, to fa yin aure ga maza ko karawa zai kara wuya, saboda yana samun biyan buƙata sai dai yayi ta tara YANMATA.


A rage buri, kwaɗayi, a tsaya a matsayin da ALLAH ya ajiye mutum, wa’ennan yana daga abinda ke kawo sa dadewa ba aure ana jiran sai kaza da kaza, daga mazan har matan, kuma ana da bukatuwa na sha’awa, to shi ke kawo irin wannan matsalar.

Post a Comment

0 Comments